Mat 21:34-37 Littafi Mai Tsarki (HAU)

34. Da kakar inabi ta kusa, sai ya aiki bayinsa wurin manoman nan su karɓo masa gallar garkar.

35. Manoman kuwa suka kama bayinsa, suka yi wa ɗaya dūka, suka kashe ɗaya, suka kuma jajjefi ɗaya.

36. Har wa yau ya sāke aiken waɗansu bayi fiye da na dā, suka kuma yi musu haka.

37. Daga baya sai ya aiki ɗansa gare su, yana cewa, ‘Sā ga girman ɗana.’

Mat 21