Mat 12:19-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. Ba zai yi husuma ko magana sama sama ba,Ba kuma wanda zai ji muryarsa tasa a titi.

20. Kyauron da ya tanƙwasa ba zai kakkarye shi ba,Fitilar da ta yi kusan mutuwa ba zai kashe ta ba,Har ya sa gaskiya ta ci nasara.

21. Al'ummai kuma za su sa zuciya ga sunansa.”

22. Sai aka kawo masa wani beben makaho mai aljan, ya kuwa warkar da shi, har beben ya yi magana, ya kuma gani.

23. Mutane duk suka yi al'ajabi, suka ce, “Shin, ko wannan shi ne Ɗan Dawuda?”

Mat 12