14. Amma Farisiyawa suka fita, suka yi shawara a kansa, yadda za su hallaka shi.
15. Da Yesu ya gane haka, ya tashi daga nan. Sai jama'a da yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da su duka.
16. Sai ya kwaɓe su, kada su bayyana shi.
17. Wannan kuwa domin a cika faɗar Annabi Ishaya ne cewa,