Mat 10:29-34 Littafi Mai Tsarki (HAU)

29. Ashe, ba gwara biyu ne kobo ba? Ba kuwa ɗayarsu da za ta mutu, ba da yardar Ubanku ba.

30. Ai, ko da gashin kanku ma duk a ƙidaye yake.

31. Kada ku ji tsoro. Ai, martabarku ta fi ta gwara masu yawa.”

32. “Kowa ya bayyana yarda a gare ni a gaban mutane, ni ma zan bayyana yarda a gare shi a gaban Ubana da yake cikin Sama.

33. Duk wanda kuwa ya yi musun sanina a gaban mutane, ni ma zan yi musun saninsa a gaban Ubanmu da yake cikin Sama.”

34. “Kada dai ku zaci na zo ne in kawo salama a duniya. A'a, ban zo domin in kawo salama ba, sai dai takobi.

Mat 10