Mak 4:8-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Yanzu fuskokinsu sun fi kukunniya baƙi,Ba a iya fisshe su a titi ba,Fatar jikinsu ta liƙe wa ƙasusuwansu,Sun bushe kamar itace.

9. Gara ma waɗanda takobi ya kasheDa waɗanda yunwa ta kashe,Gama sun rame sarai saboda rashin abinci.

10. Mata masu juyayi, da hannuwansuSuka ɗauki 'ya'yansu, suka dafa,Suka zama musu abinci a lokacin halakar mutanena.

11. Ubangiji ya saki fushinsa,Ya zuba fushinsa mai zafi.Ya kunna wa Sihiyona wutaWadda ta cinye harsashin gininta.

Mak 4