63. Suna raira mini waƙar zambo sa'ad da suke zaune,Da lokacin da suka tashi.
64. “Ya Ubangiji, za ka sāka musu bisa ga ayyukansu,
65. Za ka ba su tattaurar zuciya,La'anarka kuwa za ta zauna a kansu!
66. Da fushi za ka runtume suHar ka hallaka su a duniya, ya Ubangiji!”