Mak 3:50-58 Littafi Mai Tsarki (HAU)

50. Har lokacin da Ubangiji daga Sama ya duba, ya gani.

51. Ganin azabar 'yan matan birninaYa sa ni baƙin ciki.

52. “Waɗanda suke maƙiyana ba daliliSun farauce ni kamar tsuntsu.

53. Sun jefa ni da rai a cikin rami,Suka rufe ni da duwatsu.

54. Ruwa ya sha kaina,Sai na ce, ‘Na halaka.’

55. “Ya Ubangiji, na yi kira ga sunankaDaga cikin rami mai zurfi.

56. Ka kuwa ji muryata.Kada ka rufe kunnenka ga jin kukana na neman taimako.

57. Sa'ad da na yi kira gare ka, ka zo kusa.Sa'an nan ka ce mini kada in ji tsoro.

58. “Ka karɓi da'awata, ya Ubangiji,Ka kuwa fanshi raina.

Mak 3