10. Suna koya wa Yakubu farillanka,Suna koya wa Isra'ila dokokinka.Suna ƙona turare a gabanka,Suna ƙona hadaya ta ƙonawa a bagadenka.
11. Ya Ubangiji ka inganta jaruntakarsu,Ka karɓi aikin hannuwansu,Ka murƙushe ƙarfin abokan gābansu,Da waɗanda suke ƙinsu don kada su ƙara tashi.”
12. A kan Biliyaminu, ya ce,“Shi ƙaunatacce na Ubangiji ne,Yana zaune lafiya kusa da shi,Ubangiji yana yi masa garkuwa dukan yini,Yana zaune a kan kafaɗunsa.”