M. Sh 11:30-32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

30. Duka biyunsu suna hayin Urdun ne, yamma da hanya a ƙasar Kan'aniyawa, mazaunan Araba, kusa da Gilgal, wajen itacen oak na More.

31. Gama za ku haye Urdun, ku shiga ƙasar da za ku mallaka, wadda Ubangiji Allahnku yake ba ku. Sa'ad da kuka mallake ta, kuka zauna a ciki,

32. sai ku lura, ku aikata dukan dokoki da farillai waɗanda nake sawa a gabanku yau.”

M. Sh 11