M. Sh 1:8-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Duba, na sa ƙasar a gabanku, sai ku shiga ku mallake ta, ƙasa wadda na rantse wa kakanninku, wato Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, cewa zan ba su, su da zuriyarsu a bayansu.’ ”

9. “A wancan lokaci ne na yi magana, na ce, ‘Ba zan iya ɗaukar nawayarku ba,

10. gama Ubangiji ya riɓaɓɓanya ku, har yawanku ya kai kamar taurarin sama.

M. Sh 1