55. Amma ya juya, ya tsawata musu.
56. Sai suka ci gaba, suka tafi wani ƙauye.
57. Suna tafiya a hanya, sai wani mutum ya ce masa, “Zan bi ka duk inda za ka.”
58. Yesu ya ce masa, “Yanyawa da ramummukansu, tsuntsaye kuma da wurin kwanansu, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin shaƙatawa.”
59. Ya kuma ce wa wani, “Bi ni.” Sai ya ce, “Ya Ubangiji, ka bar ni tukuna in je in binne tsohona.”