Luk 24:15-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Ya zamana tun suna magana, suna tunani tare, sai Yesu da kansa ya matso, suka tafi tare.

16. Amma idanunsu a rufe, har ba su gane shi ba.

17. Yesu ya ce musu, “Wace magana ce kuke yi da juna a tafe?” Sai suka tsaya cik, suna baƙin ciki.

18. Sai ɗayansu, mai suna Kiliyobas, ya amsa masa ya ce, “Ashe, kai kaɗai ne baƙo a Urushalima, da ba ka san abubuwan da suka faru a can, 'yan kwanakin nan ba?”

19. Sai ya ce musu, “Waɗanne abubuwa?” Suka ce masa, “Game da Yesu Banazare ne, wanda yake annabi mai manyan ayyuka da ƙwaƙƙwarar magana a gaban Allah da dukan mutane,

Luk 24