5. Sai suka yi murna, suka kuma yi alkawarin ba shi kuɗi.
6. Shi kuwa ya yarda, ya kuma nemi hanyar bāshe shi a gare su bayan idon jama'a.
7. Sai ranar idin abinci marar yisti ta zo, wato, rana da ake yanka ɗan ragon Idin Ƙetarewa.
8. Sai Yesu ya aiki Bitrus da Yahaya, ya ce musu, “Ku je ku shirya mana Jibin Ƙetarewa mu ci.”
9. Suka ce masa, “Ina kake so mu shirya?”