9. Yā gode wa bawan nan don ya bi umarni?
10. Haka ku ma, in kuka bi duk abin da aka umarce ku, sai ku ce, ‘Mu bayi ne marasa amfani. Mun dai yi abin da yake wajibinmu kurum.’ ”
11. Wata rana yana tafiya Urushalima, sai ya bi iyakar ƙasar Samariya da Galili.
12. Yana shiga wani ƙauye ke nan, sai waɗansu kutare maza guda goma suka tarye shi, suna tsaye daga nesa.
13. Sai suka ɗaga murya suka ce, “Ya Maigida Yesu, ka ji tausayinmu,”
14. Da ya gan su, ya ce musu, “Ku je wurin firistoci su gan ku.” Suna tafiya ke nan, sai suka tsarkaka.