32. Ku tuna fa da matar Lutu.
33. Duk mai son adana ransa, zai rasa shi. Duk kuwa wanda ya rasa ransa, adana shi ya yi.
34. Ina gaya muku, a wannan dare za a ga mutum biyu a gado ɗaya, a ɗau ɗaya, a bar ɗaya.
35. Za a ga mata biyu suna niƙa tare, a ɗau ɗaya, a bar ɗaya. [
36. Za a ga mutum biyu a gona, a ɗau ɗaya, a bar ɗaya.]”
37. Sai suka amsa suka ce, “Ina ne, ya Ubangiji?” Ya ce musu, “A inda mushe yake, ai, a nan ungulai sukan taru.”