Luk 17:32-37 Littafi Mai Tsarki (HAU)

32. Ku tuna fa da matar Lutu.

33. Duk mai son adana ransa, zai rasa shi. Duk kuwa wanda ya rasa ransa, adana shi ya yi.

34. Ina gaya muku, a wannan dare za a ga mutum biyu a gado ɗaya, a ɗau ɗaya, a bar ɗaya.

35. Za a ga mata biyu suna niƙa tare, a ɗau ɗaya, a bar ɗaya. [

36. Za a ga mutum biyu a gona, a ɗau ɗaya, a bar ɗaya.]”

37. Sai suka amsa suka ce, “Ina ne, ya Ubangiji?” Ya ce musu, “A inda mushe yake, ai, a nan ungulai sukan taru.”

Luk 17