Luk 12:40-43 Littafi Mai Tsarki (HAU)

40. Ku ma sai ku zauna a kan shiri, domin a lokacin da ba ku zata ba Ɗan Mutum zai zo.”

41. Sai Bitrus ya ce, “Ya Ubangiji, mu ne kake faɗa wa wannan misali, ko kuwa na kowa da kowa ne?”

42. Ubangiji ya ce, “Wane ne amintaccen wakilin nan mai hikima, da ubangidansa zai ba shi riƙon gidansa, yă riƙa ba su abincinsu a kan kari?

43. Albarka tā tabbata ga bawan da, in ubangidansa ya dawo, zai samu yana yin haka.

Luk 12