Luk 11:37-40 Littafi Mai Tsarki (HAU)

37. Yesu yana magana, sai wani Bafarisiye ya kira shi cin abinci. Ya shiga cin abincin.

38. Sai Bafarisiyen ya yi mamakin ganin yadda Yesu zai ci abinci ba da fara wanke hannu ba.

39. Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ku Farisiyawa kam, kukan wanke bayan ƙwarya da akushi, amma a ciki cike kuke da zalunci da mugunta.

40. Ku marasa azanci! Ashe, wanda ya yi bayan, ba shi ya yi cikin ba?

Luk 11