42. har ta tā da murya da ƙarfi, ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata, ɗan cikinki kuma mai albarka ne!
43. Ta yaya wannan alheri ya same ni, har da uwar Ubangijina za ta zo gare ni?
44. Domin kuwa da jin muryarki ta gaisuwa a kunnena, sai jaririn ya motsa da ƙarfi a cikina domin farin ciki.
45. Albarka tā tabbata ga wadda ta gaskata, domin za a cika abubuwan da Ubangiji ya aiko a faɗa mata.”
46. Sai Maryamu ta ce,“Zuciyata na ɗaukaka shi, Ubangiji,