L. Mah 18:29-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

29. Suka sa wa birnin suna Dan, ɗan Yakubu. Kafin wannan lokaci kuwa ana kiran birnin Layish ne.

30. Danawa fa suka kafa gunkin domin su yi masa sujada. Jonatan, ɗan Gershom, ɗan Musa, shi da 'ya'yansa maza, suka zama firistocin Danawa, har zuwa ranar da aka kwashe mutanen zuwa bauta.

31. Haka fa suka kafa gunkin Mika har duk lokacin da alfarwar Ubangiji take a Shilo.

L. Mah 18