L. Mah 18:14-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. Mutum biyar ɗin nan da suka tafi leƙen asirin ƙasar Layish, suka ce wa abokan tafiyarsu, “Ko kun san akwai gunkin itace cikin gidajen nan? Akwai kuma gunki na zubi, da kan gida, da falmaran dominsu. Me ya kamata mu yi musu?”

15. Sai suka juya zuwa gidan Mika, inda saurayin nan Balawe yake, suka gaishe shi.

16. Danawa ɗari shida ɗin da suka yi shirin yaƙi, suka tsaya a bakin ƙofa.

17. Amma mutum biyar ɗin nan da suka tafi leƙen asirin ƙasar suka shiga kai tsaye, suka ɗauki gunkin da aka yi da itace, da falmaran, da kan gida, da gunki na zubi. Firist ɗin kuwa ya tsaya a bakin ƙofa tare da mutum ɗari shida ɗin nan masu shirin yaƙi.

L. Mah 18