7. Wato dukan biranen da za a ba Lawiyawa guda arba'in da takwas ne tare da huruminsu.
8. Isra'ilawa za su ba Lawiyawa biranen nan bisa ga girman mallakarsu. Manyan kabilai za su ba su birane da yawa, amma ƙananan kabilai za su ba su birane kaɗan.”
9. Ubangiji kuwa ya faɗa wa Musa,
10. ya ce wa jama'ar Isra'ila, “Sa'ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar Kan'ana,
11. sai ku keɓe wa kanku biranen mafaka domin wanda ya yi kisankai da kuskure, ba da niyya ba, ya gudu zuwa can.
12. Biranen za su zamar muku mafaka daga hannun mai bin hakkin jini, don kada a kashe mai kisankai tun bai riga ya tsaya a gaban shari'a ba.
13. Sai ku zaɓi birane shida.
14. Biranen mafaka uku a hayin gabashin Urdun, birane uku kuma a ƙasar Kan'ana.
15. Waɗannan birane shida za su zama wuraren mafaka ga jama'ar Isra'ila, da baƙi, da baren da yake zaune tare da su, domin duk wanda ya kashe wani ba da niyya ba, ya tsere zuwa can.