L. Kid 33:5-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Isra'ilawa kuwa suka tashi daga Ramases suka sauka a Sukkot.

6. Suka tashi daga Sukkot suka sauka a Etam wadda take a gefen jejin.

7. Da suka tashi daga Etam, sai suka juya zuwa Fi-hahirot wadda take gaban Ba'al-zefon suka sauka a gaban Migdol.

8. Da suka tashi daga gaban Fi-hahirot sai suka haye teku zuwa cikin jejin. Suka yi tafiya kwana uku a jejin Etam, suka sauka a Mara.

9. Suka tashi daga Mara suka zo Elim inda akwai maɓuɓɓugan ruwa guda goma sha biyu da itacen dabino guda saba'in. Sai suka sauka a can.

10. Suka tashi daga Elim, suka sauka a gefen Bahar Maliya.

11. Da suka tashi daga Bahar Maliya suka sauka a jejin Sin.

12. Suka tashi daga jejin Sin, suka sauka a Dofka.

L. Kid 33