L. Kid 33:46-52 Littafi Mai Tsarki (HAU)

46. Suka tashi daga Dibon-gad suka sauka a Almon-diblatayim.

47. Da suka tashi daga Almon-diblatayim, suka sauka a duwatsun Abarim a gaban Nebo.

48. Daga duwatsun Abarim suka sauka a filayen Mowab kusa da Urdun daura da Yariko.

49. Suka sauka kusa da Urdun, suka kakkafa alfarwansu tun daga Betyeshimot har zuwa Abel-shittim, a filayen Mowab.

50. Sai Ubangiji ya yi magana da Musa a filayen Mowab kusa da Urdun, daura da Yariko, ya ce

51. ya faɗa wa jama'ar Isra'ila, “Sa'ad da kuka haye Urdun zuwa ƙasar Kan'ana,

52. sai ku kori dukan mazaunan ƙasar daga gabanku ku rurrushe sassaƙaƙƙun duwatsunsu, da siffofinsu na zubi, da masujadansu.

L. Kid 33