38. Bisa ga umarnin Ubangiji, Haruna firist ya hau Dutsen Hor inda ya rasu a rana ta fari ga watan biyar a shekara ta arba'in ta fitowar jama'ar Isra'ila daga ƙasar Masar.
39. Haruna yana da shekara ɗari da ashirin da uku sa'ad da ya rasu a Dutsen Hor.
40. Sai Sarkin Arad, Bakan'ane wanda yake zaune a Negeb, a ƙasar Kan'ana, ya ji zuwan Isra'ilawa.
41. Isra'ilawa kuma suka tashi daga Dutsen Hor, suka sauka a Zalmona.
42. Daga Zalamona suka sauka a Funon.
43. Da suka tashi daga Funon, sai suka sauka a Obot.