L. Kid 25:7-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Finehas ɗan Ele'azara, wato jikan Haruna, firist, ya gani, sai ya tashi daga cikin taron, ya ɗauki mashi.

8. Ya bi Ba'isra'ilen, har zuwa ƙuryar alfarwar, ya soke dukansu biyu, Ba'isra'ilen da macen, har ya sha zarar macen. Da haka aka tsai da annoba daga Isra'ilawa.

9. Duk da haka annobar ta kashe mutane dubu ashirin da dubu huɗu (24,000).

L. Kid 25