15. Sai ya hurta jawabinsa, ya ce,“Faɗar Bal'amu ɗan Beyor,Faɗar mutumin da idonsa take buɗe,
16. Faɗar wanda yake jin faɗar Allah,Wanda ya san hikimar Maɗaukaki,Wanda yake ganin wahayin Mai Iko Dukka,Yana durƙurshe, amma idanunsa a buɗe suke.
17. Ina ganinsa, amma ba yanzu ba,Ina hangensa, amma ba kusa ba.Tauraro zai fito daga cikin Yakubu,Kandiri zai fito daga cikin Isra'ila,Zai ragargaje goshin Mowabawa,Zai kakkarya 'ya'yan Shitu duka.
18. Za a mallaki Edom,Hakka kuma za a mallaki Seyir abokiyar gābanta,Isra'ila za ta gwada ƙarfi.