L. Kid 20:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai dukan taron jama'ar Isra'ilawa suka zo jejin Zin a watan fari, suka sauka a Kadesh. A nan ne Maryamu ta rasu, a nan kuma aka binne ta.

2. Da jama'a suka rasa ruwa, sai suka taru suka tayar wa Musa da Haruna.

3. Suka ce wa Musa, “Da ma mun mutu kamar yadda 'yan'uwanmu suka mutu a gaban Ubangiji.

22-23. Sai taron jama'ar Isra'ila suka kama tafiya daga Kadesh, suka je Dutsen Hor, a kan iyakar ƙasar Edom. Ubangiji kuwa ya ce wa Musa da Haruna a can,

L. Kid 20