4. Tattarmukan da suke cikinsu kuwa suka faye kwaɗayin nama, har Isra'ilawa ma da kansu suka fara gunaguni suna cewa, “Wa zai ba mu nama mu ci?
5. Mun tuna da kifin da muka ci kyauta a Masar, da su kakamba, wato wani irin kayan lambu ne mai yaɗuwa, da guna, da sāfa, da albasa, da tafarnuwa.
6. Yanzu ranmu ya yi yaushi, ba wani abu, sai dai wannan manna muke gani.”
7. Manna kuwa kamar tsabar riɗi take, kamanninta kuwa kamar na ƙāro ne.