37. Kada ka ranta masa kuɗi da ruwa, kada kuma ka ba shi abinci don samun riba.
38. Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fanshe ku daga ƙasar Masar don in ba ku ƙasar Kan'ana, in zama Allahnku.”
39. “Idan kuwa ɗan'uwanka, Ba'isra'ile, ya talauce har ya sayar da kansa gare ka, to, kada ka bautar da shi kamar bawa.