1. Ubangiji kuwa ya yi wa Musa magana a kan Dutsen Sina'i, ya ce
2. ya faɗa wa Isra'ilawa ka'idodin nan. Sa'ad da suka shiga ƙasar da Ubangiji yake ba su, ƙasar za ta kiyaye shekara ta bakwai ga Ubangiji.
3. Shekara shida za su yi, suna ta noman gonakinsu, suna kuma ta aske gonakin inabinsu, suna tattara amfaninsu.