L. Fir 24:3-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Za a ajiye ta a gaban labulen shaida a alfarwa ta sujada. Kullum Haruna zai riƙa lura da ita daga maraice har safiya a gaban Ubangiji. Wannan zai zama muku farilla har abada a dukan zamananku.

4. Kullum sai ya shirya fitilun a bisa alkuki na zinariya tsantsa a gaban Ubangiji.

5. Ɗauki lallausan gari a toya gurasa goma sha biyu. A ki kowace gurasa da humushi biyu na garwar gari.

6. A ajiye su bisa tebur na zinariya tsantsa jeri biyu, shida a kowane jeri.

7. Sai a sa lubban tsantsa a kowane jeri don a haɗa da abincin da za a ƙone domin hadaya ta tunawa ga Ubangiji.

8. Kullum a kowace ranar Asabar, Haruna zai kintsa su a gaban Ubangiji domin Isra'ilawa saboda madawwamin alkawarin.

L. Fir 24