1. 'Ya'yan Haruna, maza, Nadab da Abihu kuwa kowannensu ya ɗauki faranti ya sa wuta, ya zuba turare a kai, ya miƙa haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji, ba irin wadda Ubangiji ya umarta ba.
2. Sai wuta ta fito daga wurin Ubangiji ta kashe su, suka mutu a gaban Ubangiji.