K. Mag 9:12-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. Kai ne da riba in ka sami hikima. Kai za ka sha hasara in ka ƙi ta.

13. Wawanci kamar mace ce mai kwakwazo, jahila, marar kunya.

14. Takan zauna a ƙofar gidanta, ko a wurin da ya fi duka bisa a cikin gari.

15. Takan yi ta kiran masu wucewa waɗanda hankalinsu yake a kan ayyukansu, ta ce,

16. “Ku shigo, ku jahilai!” Takan ce wa dolo,

17. “Ruwan da aka sata ya fi daɗi, haka nan kuma abincin da ake satar ya fi daɗi.”

K. Mag 9