8. Ka ƙaunaci hikima, za ta girmama ka. Ka rungume ta, za ta kawo maka daraja.
9. Za ta zamar maka rawanin daraja.”
10. Ɗana, ka kasa kunne gare ni. Ka ɗauki abin da nake faɗa maka, muhimmin abu ne, za ka yi tsawon rai.
11. Gama na koya maka hikima da hanyar zama mai kyau.
12. Idan ka yi tafiya da hikima ba abin da zai tsare maka hanya, sa'ad da kake gudu ba za ka yi tuntuɓe ba.