19. Kada ka damu saboda mugaye, kada ka yi ƙyashin masu aikata abin da ba daidai ba.
20. Gama mugun mutum ba shi da sa zuciya, ba abin da zai sa zuciya a kansa nan gaba.
21. Ɗana, ka yi tsoron Ubangiji, ka kuma ji tsoron sarki, kada ka yi harkar kome da mutanen da suka tayar musu.
22. Irin waɗannan mutane sukan hallaka farat ɗaya. Ka taɓa yin tunani a kan bala'in da Allah ko sarki sukan aukar?
23. Masu hikima kuma sun faɗi waɗannan abu.Kuskure ne alƙali ya yi son zuciya.
24. Idan ya kuɓutar da mugu, kowane mutum da yake a duniya zai la'anta shi ya ƙi shi.
25. Alƙalan da suke hukunta wa mai laifi kuwa, za su arzuta, su ji daɗin kyakkyawan suna.
26. Amsar gaskiya ita ce alamar abuta ta ainihi.
27. Kada ka gina gidanka ka kafa shi, sai ka gyara gonakinka, ka tabbata za ka sami abin zaman gari.