K. Mag 18:18-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Idan mutum biyu ƙarfafa suna jayayya da juna a gaban shari'a, kuri'a a asirce kaɗai take iya daidaita tsakaninsu.

19. Ɗan'uwan da ya ji haushinka zai gagare ka, idan ka yi faɗa da shi zai rufe maka ƙofarsa.

20. Bisa ga sakamakon hurcinka haka za ka rayu.

21. Abin da ka faɗa ya iya cetonka ko ya hallaka ka, saboda haka tilas ne ka karɓi sakamakon maganarka.

22. Idan ka sami mace ka sami abu mai kyau, wannan alheri ne wanda Ubangiji ya yi maka.

K. Mag 18