24. Sai suka amsa wa Joshuwa, suka ce, “Domin bayinka sun ji labari Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa ya ba ku ƙasar duka, ku hallaka dukan mazaunan ƙasar a gabanku, don haka muka ji tsoronku ƙwarai saboda rayukanmu, shi ya sa muka yi haka.
25. Yanzu dai muna a hannunka, ka yi yadda ka ga ya yi maka kyau.”
26. Haka kuwa ya yi musu, ya cece su daga hannun Isra'ilawa, har ba su kashe su ba.