Ish 63:6-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Da fushina na tattake dukan sauran al'umma, na farfashe su. Na kwararar da jinin ransu a ƙasa.”

7. Zan faɗi ƙaunar Ubangiji marar ƙarewa,Zan yabe shi saboda dukan abin da ya yi mana.Ya sa wa jama'ar Isra'ila albarka mai yawa,Saboda jinƙansa da ƙaunarsa marar matuƙa.

8. Ubangiji ya ce, “Su mutanena ne, ba za su ruɗe ni ba.” Saboda haka kuwa ya cece su

9. daga dukan wahalar da suke sha. Ba mala'ika ne ya cece su ba, amma Ubangiji ne. Da ƙaunarsa da juyayinsa ya fanshe su. A koyaushe yake lura da su a dā,

10. amma suka i masa tayarwa, suka cika shi da ɓacin rai. Saboda haka Ubangiji ya yi gāba da su, ya kuwa yi yaƙi da su.

11. Amma suka tuna da zamanin dā, zamanin Musa bawan Ubangiji, suka yi tambaya suka ce, “Yanzu fa, ina Ubangiji yake wanda ya ceci shugabannin jama'arsa daga teku? Ina Ubangiji yake, wanda ya ba Musa iko musamman?

Ish 63