3. Ubangiji ya amsa ya ce, “Na tattake al'ummai kamar 'ya'yan inabi, ba kuwa wanda ya taimake ni. Na tattake su cikin fushina, jininsu kuwa ya fantsamar wa dukan tufafina.
4. Na ga lokacin da zan fanshi mutanena ya yi, lokaci ne da zan hukunta wa abokan gābansu.
5. Na yi mamaki sa'ad da na duba, sai na ga ba wanda zai taimake ni. Amma fushina ya sa na sami ƙarfi, har ni kaina na ci nasara.
6. Da fushina na tattake dukan sauran al'umma, na farfashe su. Na kwararar da jinin ransu a ƙasa.”
7. Zan faɗi ƙaunar Ubangiji marar ƙarewa,Zan yabe shi saboda dukan abin da ya yi mana.Ya sa wa jama'ar Isra'ila albarka mai yawa,Saboda jinƙansa da ƙaunarsa marar matuƙa.