3. Ubangiji ya ce wa jama'arsa,“Ba a biya kuɗi domin a saye ku ba,Amma ga shi, kuka zama bayi.Ba za a biya kuɗin fansa domin a 'yantar da ku ba,Amma, ga shi, za a 'yantar da ku.
4. Kuka taɓa zaman baƙuntaka a Masar,Daga baya Assuriyawa suka zalunce ku ba gaira ba dalili.
5. Yanzu kuma, ga shi, yana faruwa a Babila,Kuka zama kamammu a can, ba gaira ba dalili.Su da suke mulkinku suna girmankai, suna fāriya,Suna ta nuna mini raini.
6. Amma zuwa gaba za ku saniNi ne Allah, wanda na yi magana da ku.”