Ish 52:2-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. Ki kakkaɓe kanki, ya Urushalima!Ki tashi daga cikin ƙura,Ki hau gadon sarautarki.Ki ɓaɓɓale sarƙoƙin da suke ɗaure da ke,Ke kamammiyar jama'ar Sihiyona!

3. Ubangiji ya ce wa jama'arsa,“Ba a biya kuɗi domin a saye ku ba,Amma ga shi, kuka zama bayi.Ba za a biya kuɗin fansa domin a 'yantar da ku ba,Amma, ga shi, za a 'yantar da ku.

4. Kuka taɓa zaman baƙuntaka a Masar,Daga baya Assuriyawa suka zalunce ku ba gaira ba dalili.

Ish 52