2. Ki kakkaɓe kanki, ya Urushalima!Ki tashi daga cikin ƙura,Ki hau gadon sarautarki.Ki ɓaɓɓale sarƙoƙin da suke ɗaure da ke,Ke kamammiyar jama'ar Sihiyona!
3. Ubangiji ya ce wa jama'arsa,“Ba a biya kuɗi domin a saye ku ba,Amma ga shi, kuka zama bayi.Ba za a biya kuɗin fansa domin a 'yantar da ku ba,Amma, ga shi, za a 'yantar da ku.
4. Kuka taɓa zaman baƙuntaka a Masar,Daga baya Assuriyawa suka zalunce ku ba gaira ba dalili.