24. Kuna iya ku ƙwace wa sojoji wason da suka yi?Kuna iya kuɓutar da 'yan kurkuku daga ɗaurin masu baƙin mulki?
25. Ubangiji ya amsa ya ce,“Wannan shi ne ainihin abin da zai faru.Za a ƙwace kamammun yaƙi,Za a kuma ƙwace wason da masu baƙin mulki ya yi.Zan yi yaƙi da dukan wanda yake yaƙi da ku,Zan kuwa kuɓutar da 'ya'yanku.
26. Zan sa masu zaluntarku su karkashe juna,Za su yi māye, da kisankai, da fushi.Sa'an nan dukan 'yan adam za su sani, ni ne Ubangiji,Wanda ya cece ku, ya fanshe ku.Za su sani ni ne Allah Mai Iko Dukka na Isra'ila.”