12. Mutanena za su zo daga can nesa,Daga Birnin Sin a kudu,Daga yamma, da arewa.”
13. Ku raira, ku sammai! Ki yi sowar murna, ke duniya!Bari duwatsu su ɓarke da waƙa!Ubangiji zai ta'azantar da mutanensa,Zai ji juyayin mutanensa da suke shan wahala.
14. Amma mutanen Urushalima suka ce,“Ubangiji ya yashe mu!Ya manta da mu.”
15. Saboda haka Ubangiji ya amsa ya ce,“Mace za ta iya mantawa da jaririnta,Ta kuma ƙi ƙaunar ɗan da ta haifa?Ya yiwu mace ta manta da ɗanta,To, ni ba zan taɓa mantawa da ku ba.
16. Ya Urushalima, ba zan taɓa mantawa da ke ba,Na rubuta sunanki a gabana.