Ish 41:26-29 Littafi Mai Tsarki (HAU)

26. Wane ne a cikinku ya faɗa mana tun da wuri,Ko ya yi annabci, cewa wannan zai faru,Har da za mu ce kun yi daidai?Ba ko ɗayanku da ya ce tak a kan wannan,Ba kuwa wanda ya ji kuna faɗar wani abu!

27. Ni Ubangiji, ni ne na farko da na faɗa wa Sihiyona albishir,Na aiki manzo zuwa Urushalima don ya ce,‘Jama'arki suna zuwa! Suna zuwa gida.’

28. Sa'ad da na duba alloli,Ba wanda yake da abin da zai faɗa,Ko ɗaya, ba wanda ya iya amsa tambayar da na yi.

29. Dukan waɗannan alloli ba su da amfani,Ba su iya kome ba, ko kaɗan,Gumakansu ba su da ƙarfi, ba su kuma da iko!”

Ish 41