Ish 3:9-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. Ayyukansu na son zuciya za su zama shaida gāba da su. Suna ta aikata zunubi a fili, kamar yadda mutanen Saduma suka yi. Sun shiga uku, su ne kuwa suka jawo wa kansu.

10. Adalai za su yi murna, kome zai tafi musu daidai. Za su ji daɗin abin da suka aikata.

11. Amma mugaye sun shiga uku, za a sāka musu bisa ga abin da suka aikata.

12. Masu ba da rance da ruwa suna zaluntar jama'ata, masu ba da bashi kuwa suna cutarsu.Ya jama'ata, shugabanninku a karkace suke bi da ku, saboda haka ba ku san inda za ku nufa ba.

Ish 3