Ish 25:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ya Ubangiji, kai ne Allahna, Zan ɗaukaka ka, in yabi sunanka.Ka aikata al'amura masu banmamaki,Ka tafiyar da su da aminci,Wato bisa ga shirin da ka yi tuntuni.

2. Ka mai da birane kufaiKa lalatar da kagaransu,Wuraren da maƙiya suka gina kuwa,An shafe su har abada.

3. Jama'ar al'ummai masu iko za su yabe ka,Za a ji tsoronka a biranen mugayen al'ummai.

Ish 25