12. A wannan rana, Ubangiji Mai Runduna zai ƙasƙantar da kowane mai iko, da kowane mai girmankai, da kowane mai fāriya.
13. Zai hallaka dogayen itatuwan al'ul na Lebanon, da dukan itatuwan oak na ƙasar Bashan.
14. Zai baje duwatsu da tuddai masu tsayi,
15. da kowace doguwar hasumiya, da ganuwar kowace kagara.
16. Zai nutsar da jiragen ruwa mafi girma mafi kyau.
17. Girmankan ɗan adam zai ƙare, za a hallakar da fāriyar ɗan adam, Ubangiji ne kaɗai za a ɗaukaka sa'ad da wannan rana ta yi,