2. Ikon Ubangiji zai ba shi hikima,Da sani, da gwaninta yadda zai mallaki mutanensa.Zai kuwa san nufin Ubangiji, ya kuma yi tsoronsa,
3. Zai ji daɗin yin hidimarsa.Ba zai yi shari'ar ganin ido ko ta waiwai ba.
4. Zai yi wa matalauta shari'a daidai.Zai kuma kāre hakkin masu tawali'u.Bisa ga umarninsa za a hukunta ƙasar,Mugaye za su mutu.
5. Zai yi mulkin mutanensa da adalci da mutunci.