12. Kunyarku ta kai cikin sauranal'umma,Kukanku kuma ya cika duniya.Soja na faɗuwa bisa kan soja.Dukansu biyu sun faɗi tare.
13. Ubangiji ya yi magana da Irmiya a kan zuwan Nebukadnezzar, Sarkin Babila, don ya yi yaƙi da ƙasar Masar.
14. “Ku yi shelarsa cikin garuruwanMasar,Cikin Migdol, da Memfis, daTafanes,Ku ce, ‘Ku tsaya, ku yi shiri,Gama takobi yana cin waɗanda sukekewaye da ku!’
15. Me ya sa gunkinka, Afis, ya fāɗi,Wato bijimi, gunkinka bai tsaya ba?Domin Ubangiji ya tunkuɗe shiƙasa!
16. Sun yi ta fāɗuwa,Suna faɗuwa a kan juna,Sai suka ce, ‘Mu tashi mu komawurin mutanenmu,Zuwa ƙasar haihuwarmu, mu gududaga takobin azzalumi!’
17. “Ku ba Fir'auna Sarkin Masarsabon suna,‘Mai yawan surutu, wanda bai rifcizarafi ba!’
18. Ni wanda sunana Ubangiji MaiRunduna Sarki ne,Na rantse da raina, wani zai ɓullo,Kamar Tabor a cikin tsaunuka,Ko kuwa kamar Karmel a bakinteku.
19. Ya ku mazaunan Masar,Ku shirya kayanku don zuwa bauta,Gama Memfis za ta lalace, ta zamakufai,Ba mai zama a ciki.
20. “Masar kyakkyawar karsana ce,Amma bobuwa daga arewa ta aukarmata!