Irm 2:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji ya ce mini,

2. in tafi in yi shelar abin da Ubangiji ya ce a kunnen Urushalima, in ce,“Na tuna da amincinki a lokacinƙuruciyarki,Da ƙaunarki kamar ta amarya daango.Yadda kika bi ni a cikin jeji, da aƙasar da ba a shuka ba.

3. Isra'ila tsattsarka ce ta Ubangiji,Nunar fari ta girbina.Dukan waɗanda suka ci daga cikinkisun yi laifi,Masifa za ta auko miki.Ni Ubangiji, na faɗa.”

4. Ku ji jawabin Ubangiji, ku zuriyar Yakubu, ku dukan kabilan Isra'ila.

Irm 2